Connect with us

Ƙetare

Yan tawayen  M23 na ci gaba da tilastawa fararen hula tserewa daga Gabashin Congo

Published

on

Harin ‘yan tawayen  M23 na ci gaba da tilastawa fararen hula tserewa daga Gabashin Jamhuriyar Dumokaradiyyar Congo da birnin Sake da ke Gabashin kasar  ke  ci gaba da kasancewa cikin tashin hankali da fargaba sakamakon rikicin dake faruwa tsakanin dakarun gwamnati da ‘yan tawaye.

 

Birnin ya kasance wata babbar cibya mai mahimmanci wajen kare birnin Goma, babban birnin lardin Kivu ta Arewa.

 

Rahotanni daga ƙungiyoyin kare hakkin bil’adama sun nuna cewa ‘yan tawayen M23 sun tilastawa dubban mutane barin gidajensu a garin Sake, inda aka kora su zuwa birnin Goma.

 

Duk da cewa an ƙulla yarjejeniyoyin tsagaita wuta tsakanin gwamnati da ‘yan tawayen  a kasashen Qatar da Amurka, faɗan ya ci gaba da ƙazanta tare da amfani da makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuka  kan fararen hula.

 

Rikicin ya tilastawa miliyoyin mutane barin muhallan su a sassan gabashin Congo, inda mutane da dama ke rayuwa a sansanonin ‘yan gudun hijira cikin mawuyacin hali.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!