Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yanzu -yanzu: kwale-kwele ya kife da Ɗaliban islamiyya a Kano

Published

on

Wani kwale-kwele ɗauke da ɗaliban makarantar Islamiyya ya nutse a ƙaramar hukumar Ɓagwai.

lamarin ya haifar da mutuwar ɗalibai 10 yayin da sama da ɗalibai 30 suka ɓace a ruwan.

Wani shaidar gani da ido ya tabbatarwa da Freedom Radio cewa, sama da ɗalibai 24 an samu nasarar ceto su da yammacin ranar Talata.

Tun da fari dai an gano gawarwakin mutane 10 da suke shawagi a saman ruwan da ke madatsar ruwa ta Bagwai a karamar hukumar Bagwai a jihar Kano.

Rahotanni sun ce jirgin na dauke ne da daliban Islamiyya daga kauyen Badau zuwa Bagwai domin bikin Mauludi.

Cikakken bayani zai zo daga baya

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!