Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

COVID-19 :  Ana daf da bude makarantun Islamiyya a Kano

Published

on

Hukumar Kula da Makarantun Islamiyya ta jihar Kano ta bukaci Malaman Islamiyya da dalibai da su kara hakuri don kuwa gwamnati na dab da kammala tattaunawa da jami’an lafiya domin bude Makarantu baki daya.

Shugaban hukumar Sheikh Gwani Yahuza Gwani Danzarga ne ya bayyana haka a yayin da yake zantawa da manema labarai a nan Kano.

Sheikh Gwani Yahuza ya kara da cewa gwamnatin Jihar Kano, ta damu matuka ganin yadda daliban ke zaune a cikin gidajensu, ba tare da karatun Addini da na Islamiyya ba.

Shehin Malamin ya kuma ce,annoba gaskiya ce saboda hakane ma All.. yayi umarnin cewa duk lokacin da annoba ta bullo to wajibi ne a dauki matakan kariya domin kare al’umma.

Labarai masualaka : 

Babu wanda ya rasa ran sa a cikin masu dauke da cutar Corona a Kano

Ganduje ya fara daukar Malaman da zasu yi koyarwa a makarantun Tsangayu

Wakilinmu Bilal Nasidi Mu’azu ya ruwaito cewa, shugaban hukumar na kira ga al’umma da su ci gaba da bin dokokin da jami’an lafiya suka shinfida musu.

 

 

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!