Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yau Malam Aminu Kano ke cika shekaru 38 da rasuwa

Published

on

An haifi Malam Aminu Kano a ranar 9 ga watan Augusta 1920 a unguwar Sudawa da ke yankin karamar hukumar Gwale a birnin Kano.

 

Malam Aminu Kano ya halarci kwalejin Katsina kafin daga bisani ya zarce zuwa sashen nazarin ilimi da ke jami’ar London shi da tsohon firaministan Najeriya, Sir Abubakar Tafawa Balewa.

 

Malam Aminu Kano ya samu takardar shaidar koyarwa a jami’ar London, inda ya zama malami ya kuma koyar a kwalejin horas da malamai da ke Bauchi.

 

Lokacin da ya ke koyarwa a Bauchi ya shahara wajen sukar salon mulkin turawan mulkin mallaka.

 

A shekarar 1943 shida Sa’adu Zungur da Abubakar Tafawa Balewa suka kafa wata kungiyar siyasa da ake wa lakabi da BAUCHI Bauchi General Improvement Union.

 

A shekarar 1948 ne kuma ya zama shugaban makarantar Maru da ke jihar Sokoto sannan aka zabe shi a matsayin sakataren kungiyar malaman arewacin Najeriya.

 

Lokacin da ya ke zaune a Sokoto ya ba da gudunmawa wajen bunkasa ilimin Qur’ani a makarantu.

 

Haka kuma a Sokoton ne ya shiga Jam’iyyar Mutanen Arewa, wanda ita ce daga bisani ta rikide ta zama jam’iyyar NPC.

 

Malam Aminu Kano ya balle daga jam’iyyar NPC, inda shi da wasu ‘yan gwagwarmaya suka kafa jam’iyyar NEPU.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!