Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za a baiwa Ibrahim Magu jerin zarge-zargen da ake masa a rubuce

Published

on

Kwamitin shugaban kasa da ke binciken dakataccen shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC karkashin jagorancin tsohon shugaban kotun daukaka kara mai shari’a Ayo Salami, ya amince ya bai wa Ibrahim Magu kwafin bayanan zarge-zargen da a ke yi masa.

Tun farko dai kwamitin shugaban kasa da ke binciken kadarorin gwamnati ne ya zargi Ibrahim Magu ta cikin wani rahoto da ya mikawa ofishin attorney janar na kasa kuma ministan shari’a.

Sai dai rahotanni sun ce shugaban kwamitin Justice Ayo Salami ya shaidawa lauyan Ibrahim Magu Barista Wahab Shittu cewa za a basu kwafin rahoton amma da yarjejeniyar ba za a bari ‘yan jarida su gani ba.

Rahotanni sun ce a yau alhamis ake sa ran Ibrahim Magu zai fara kare kansa gaban kwamitin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!