Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za a janye ‘yan sandan dake aiki a EFCC

Published

on

Babban sufeton ‘yan sandan kasar nan Muhammad Adamu ya bada umarnin janye dukannin ‘yan sandan da ke aiki a hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da aka aikewa da mataimakan sufeto janar na ‘yan sanda da kuma ‘yan sandan kwantar da tarzoma da sauran su, ana kuma basu umarnin su janye dukannin ‘yan sandan da ke aiki a hukumar ta EFCC.

Umarnin ya kuma tafi ne da kunshin hana duk wani mutum shiga harabar hukumar ta EFCC banda ma’aikatan ta, kuma ya zama wajibi ‘yan sandan da ke aiki a hukumar su koma shalkwatar rundunar da ke birnin tarayya Abuja da misalin karfe 8 na safiyar ranar Litinin mai zuwa.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!