Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Jigawa

Za a kafa dokar hukuncin kisa ga masu fyaɗe ba tare da zaɓin tara ba a jihar Jigawa

Published

on

Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kafa dokar hukuncin kisa ga duk wanda aka kama da laifin yi wa ƙaramar yarinya fyaɗe, a wani mataki na tabbatar da kare kananan yara.

Kwamishinan harkokin shari’a na Jihar Dr Musa Adamu ne ya sanar da hakan jiya, yayin taron manema labarai na ƙarshen shekara da ya gudanar a birnin Dutse.

Dr Musa Adamu ya ce duk wanda aka kama da yi wa ƙaramar yarinya ‘yar ƙasa da shekaru goma fyade a jihar to haƙiƙa hukuncin kisa ya tabbata a kansa, ba tare da zaɓin ɗaurin rai-da-rai ba.

Tun a farkon shekarar nan ce gwamnan Jihar ta Jigawa Alhaji Muhammad Badaru ya sanya hannu kan dokar kare kananan yara, wadda ta yi tanadin hukuncin kisa kan masu fyaden, amma kuma da zabin daurin rai-da-rai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!