Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za a rika bude Kano sau biyu a sati -Ganduje

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce zata rika bude gari a lokacin nan na zaman gida a duk ranar litinin da alhamis daga karfe goma na safe zuwa hudu na yamma kowacce rana.

Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne a yau asabar da yake zantawa da manema labarai.

Ya kuma ce ba za a bude kasuwanni ba sai dai kasuwannin Yanlemo da Yan kaba ne kadai aka yadda su bude suma daga karfe goma na safe zuwa hudu na yammar kowacce litinin da alhamis din ranakun.

Ya kuma kara da cewa Alhaji Aliko Dangote ya Samar da cibiyar gwajin cutar ta tafi da gidan ka da zata rika gwada mutane Dari hudu kowacce rana.

Wakiliyar mu Zahrau Nasir ta ruwaito cewa mataimakin Gwamnan Nasir Gawuna yace za a Samar da cubiyoyin gwajin cutar Corona nan bada dadewa ba a dukkan kananan hukumomi 44 na jihar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!