Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

An bude sabuwar cibiyar gwajin Corona da Dangote ya samarwa Kano

Published

on

Gidauniyar Aliko Dangote ta damkawa gwamnatin Kano cibiyar gwajin cutar Corona ta tafi da gidanka da ta samar a asibitin Muhammadu Buhari dake Giginyu.
Cibiyar gwajin za ta rika gwada mutane 400 a kullum, sannan bayan mako daya ta gwada mutum 1000 a rana.
A yayin taron mika cibiyar gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya godewa Alhaji Aliko Dangote bisa ga wannan al’amari na wannan namijin kokari da yayi.
A nata bangren Dakta Zuwaira Yusuf wacce itace shugabar gidauniyar Dangote tace sunyi wannan taimakon ga Kano ne duba da irin samun karin masu cutar da ake samu a Kano.

Gwamna Ganduje yayin raba takardun daukan aiki ga sabbin malamai 25-02-2020

Da yake jawabi shugaban tawagar likitoci da aka turo Kano daga gwamnatin tarayya Dakta Nasir Sani Gwarzo ya ce an fara bincike domin gano abinda ya jawo yawaitar mace-mace a Kano.
Wakiliyar mu Zahra’u Nasir ta rawaito cewa daga cikin masu taron sun hada da shugaban cibiyar dakile cutuka masu yaduwa ta Kasa NCDC Chikwe Ihekuezo.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!