Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu ɗaukaka ƙara kan hurumin kotu na rushe shugabancin Abdullahi Abbas – Ganduje

Published

on

Gwamnatin Kano ta ce za ta ɗaukaka kara a kan hukuncin da kotu a Abuja ta yi na rushe zaɓen tsagin gwamna Ganduje da aka yi na shugabannin jam’iyyar APC a nan Kano.

Kwamishinan shari’a Barista Musa Abdullahi lawan ne ya bayyana hakan a yau yayin ganawa da manema labarai, jim kadan bayan da kotun ta sanar da hukuncinta kan zaɓen.

Barista Musa Lawan ya ce “za mu duba kundin tsarin shari’a domin ɗaukar matsaya tare da yin duba, don ganin kotun na da hurumi ko ba ta da hurumi a kan shari’ar”.

“Ko a lokacin da aka yi zaɓen mazabu  na Kano a guda ɗaya aka yi, a don haka za mu duba hukuncin tare da ɗaukar mataki a nan kusa”.

A ranar Talata 30 ga watan Nuwamba wata babbar kotu a Abuja ta rushe zaɓen da aka yiwa shugaban jam’iyya APC tsagin gwamnan Kano Dakta Abdullahi Ganduje.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!