Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu baza jami’ai 1,500 don tabbatar da doka a bikin Sallah- KAROTA

Published

on

Hukumar kula da zirga zirgar ababen hawa ta jihar KAROTA, za ta baza jami’anta guda 1,500 domin sanya ido a shagulgulan bikin Sallah.

Hukumar ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta Nabilusi Abubakar Kofar Na’isa, ya fitar yau Litinin.

Ta cikin sanarwar, hukumar ta KAROTA, ta ce, za ta rarraba jami’an nata ne domin su tabbatar da bin dokokin tuki a yayin bukukuwan na Sallah.

Haka kuma hukumar ta ja hankalin jama’a da su kiyaye tare da bin doka sau da ķafa domin guje wa hadura a lokacin bikin Sallah.

Hukumar ta ce, ta haramta yin guje-guje da ababen hawa da wasu ke yi, wadanda hakan ke zama barazana ga rayuwar al’umma

KAROTA, ta kuma ja hankalin iyaye da su guji bai wa yaran da suke kasa da shekaru 18 tukin ababen hawa, domin kuwa hukumar ba za ta lamunci hakan ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!