Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu yi bincike kan gine-gine da filayen da aka yanka a Dawakin Tofa- Kantoma

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta umarci duk wani wanda yasan ya fara gini ko yanka gonaki da suke mallakin gwamnati a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa ya dakata domin gwamnati zata gudanar da binciken yadda aka mallaka musu.

Shugaban ƙaramar hukumar na riƙo Kabiru Ibrahim Danguguwa, ne ya bayyana hakan yayin rabon tallafin kuɗi ga dukkan nin shugabancin ƙaramar hukumar domin samar musu da abin da zasu gudanar da bikin sallah.

Kabiru Danguguwa ya kuma ce wannan mataki na dakatar da duk wasu masu gine-gine ko yanka gonaki da filaye Asibitoci da makarantu ya biyo bayan bincike da gwamnatin Kano zatayi kan yadda gwamnatin baya ta mallakawa su gurare mallakin gwamnati.

Ɗanguguwa ya ƙara da cewa yanzu haka gwamnati jihar kano ta samar da wani kwamiti wanda zaiyi binciken yadda akayi tasarrafi da filaye da gonakin gwamnati a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa.

Haka kuma zamu ɗau mataki ga duk wanda muka samu da yin kunnen ƙashi wajen ƙin dakatar da gini ko yanka filaye a yankin, A cewar Ɗanguwa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!