Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu ci gaba da kyautata dangantaka da kasar Indiya – Ganduje

Published

on

Gwamantin Kano ta ce zata cigaba da kyautata alakar ta da Kasar Indiya wacce aka jima ana yin ta.

Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana hakan ne lokacin da ya ke karbar bakuncin karamin jakadan Kasar Indiya a Najeria a fadar gwamnatin Kano.

Ganduje ya ce dama dai akwai kyakyawar alaka tsakanin kasar ta Indiya da Najeriya sannan yace zata cigaba da dorewa tsakanin gwamnatin Kano ta fannoni daban-daban.

Yana mai cewa, alakar zata cigaba a fannin kayayyakin amfanin noma daga kasar Indiya kasancewar manoman jihar Kano na yabawa da kayayyakin nasu.

Wakiliyar mu ta fadar gwamnatin Kano Zahrau Nasir ta ruwaito cewa, karamin jakadan na kasar Indiyar a Najeriya Abay Takur ya Kuma ce ya kawo ziyarar ne shi da tawagar sa don Kara inganta alaka da jihar Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!