Connect with us

Labarai

Za mu tsaurara matakan tsaro a gidajen gyaran hali na Zamfara – CP Ayuba Elkanah

Published

on

Kwamishinan ƴan sanan jihar Zamfara Ayuba Elkanah ya ziyarci gidan gyaran hali na Gusau babban birnin jihar.

Ziyarar ta sa ta mayar da hankali wajen duba yadda tsaro ke kasancewa a gidajen gyaran hali na jihar da kuma magance duk wani barazanar tsaro.

Mai magana da yawun runudanar ƴan sanda Muhammad Shehu ne ya tabbatar da hakan ta cikin wata sanarwa.

Ya ce, ziyarar ta Ayuba Elkanah za ta mayar da hankali wajen nazartar yadda sha’anin tsaro yake a gidajen, da yunƙurin ƙara inganta tsaron.

Ta cikin sanarwar, Ayuba Elkanah ya tabbatar da cewa za a ƙara tsaurara matakan tsaro a gidajen gyaran halin da ke fadin jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!