Connect with us

Labarai

Za mu yi luguden wuta ta sama domin kakkaɓe ƴanbindiga a Najeriya:

Published

on

Babban hafsan sojin saman Najeriya, Air Marshal Sunday Aneke, ya bayar da umarni ga kwamandojin da ke lura da jiragen yaƙi su tsananta hare-hare kan maɓoyar ƴanbindiga a ƙasar.

Aneke ya bayyana hakan ne a lokacin wani taron da ya jagoranta tsakanin manyan kwamandojin da ke jagorantar rundunonin da ke yaƙi da ƴanbindiga a ƙasar

Taron ya tattauna sabbin dabarun da rundunar za ta ɓullo da su wajen kai hare-hare kan maɓaiyar ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya.

Sanarwar bayan da taron da rundunar sojin saman ta fitar, ta ce a ganawar manyan dakarun an ɓullo da dabarun haɗin gwiwa tsakanin rundunar sojin saman da sauran rundunonin tsaron.

Matakin na zuwa ne mako guda bayan da Shugaba Bola Tinubu ya rantsar da sabbin shugabannin rundunonin sojin ƙasar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!