Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Katsina ta za ta dauki tsauraran matakai kan ‘yan ta’adda

Published

on

Gwamnatin jihar Katsina ta ce daga yanzu babu sauran sasanci tsakaninta da masu aikata ta’addanci a jihar.

Haka zalika gwamnatin ta Katsina ta nemi gwamnatin tarayya da ta dauki matakai kan matsalolin ‘yan bindigar da suka addabi wasu jihohin Arewa ciki har da Katsinan.

Sakataren gwamnatin jihar Mustapha Muhammad Inuwa a zantaawrsa da Freedom radio ya ce sun lura cewa ‘yan ta’addar da suka cimma yarjejeniyar zaman lafiya da su a baya sun koma ruwa.

Ya ce ya kamata gwamnatin tarayya ta dauki mataki mai tsauri a kan ‘yan ta’addar, la’akari da yadda suke neman mamaye wasu jihohin.

“A tunkari mutanen nan gaba-daya, a shiga Katsina, zamfara, Kaduna, Neja a tabbatar an yi musu zobe, ina me tabbatar maka yin hakan zai taimaka wajen shawo kan matsalar ta’addancin nan”. In ji shi

A cewarsa ya fi kyautuwa a kara kaimi a yaki da ta’addanci, domin mutanen yankunan da abun ya shafa su samu su koma muhallansu.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!