Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

Zafin ciwo ya sanya wani mutum fede cikin sa da wuka a Kaduna

Published

on

Wani magidanci a jihar Kaduna ya fede cikin sa da wuka sanadiyyar zafin cutar gyambon ciki wato (Ulcer) dake damun sa.

Wannan al’amari dai ya faru ne, a garin Lere dake jihar Kaduna inda magidancin mai suna Hashim Muhammad ke fama da cutar ulcer wanda zafin ciwon ta ya sanya, yayi amfani da wuka wajen fede cikin sa.

Wakilin Freedom Radio Haruna Ibrahim Idris ya samu tattaunawa da Aisha Muhammad wadda kanwa ce ga mutumin, wadda ta ce ya jima yana fama da cutar ta ulcer, sai dai a wannan karon abin ya zo da zafi.

Yanzu haka dai Hashim Muhammad na kwance a gadon babban asibitin garin Lere, cikin mawuyacin hali, inda yake samun kulawar jami’an lafiya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!