Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zamu ƙarawa limamai kuɗin Alawus ɗin da ake basu

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce zata ƙarawa dukkan nin limaman masallatan juma’a kuɗin da ake basu a wata la’akari da yadda abin da ake biyan su yayi kaɗan.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da limaman masallatan juma’a dake faɗin jihar Kano.

Gwamna Yusuf ya ce la’akari da irin gudunmawar da limaman suke bayarwa ga addinin musulunci ya sanya gwamnatin jihar Kano zatayi wannan huɓɓasa wajen ƙara musu alawus ɗin da ake basu.

Haka zalika Gwamnan ya buƙaci malaman Addinin musuluncin da ke faɗin jihar kano da su mayar da hankali wajen faɗakar da al’umma abin da addini ya tanadar domin kawowa jihar kano ci gaba.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kuma ce yawan faɗakar da al’umma da malamai sukeyi na taka muhimmiyar rawa wajen samar da tarbiyyar al’umma.

Haka kuma gwamnan ya ce wannan ƙarin kuɗin da gwamnati zatayiwa limaman zaizo ne kai tsaye daga ofishin babban akantan kuɗi na jihar

Wasu daga cikin limaman masallatan juma’a dake nan kano sun wannan abu da gwamna zaiyi musu abin a yaba ne.

Wanda hakan zai ƙara karfafa musu gwiwa da ci gaba da gudanar da aikin su yadda ya kamata.

Haka kuma gwamnan ya ce yanzu haka ya sanya kwamitin da zai sanya idanu wajen kula da ciyarwar azimin watan Ramadana domin samarwa da al’umma sassaucin matsin da ake ciki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!