Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zargin badakala: Majalisar wakilai ta yi barazanar kama shugabannin kamfanin NNPC

Published

on

Majalisar wakilai ta bai wa wasu hukumomi goma sha bakwai da ke karkashin kamfanin mai na kasa (NNPC) wa’adin mako guda da su gurfana gaban kwamitinta da ke kula da asusun gwamnati don tattauna wasu al’amura da suka shige duhu ga ‘yan majalisar.

A cewar majalisar gaza bayyanan jami’an gaban kwamitin zai sanya taga ba ta da zabi da ya wuce ta ba da umarnin kama shugabannin hukumomin don gurfanar da su.

A kwanakin baya ne dai ofishin babban mai binciken kudi na tarayya ya aika da takardar tuhuma ga hukumomin sakamakon gaza fayyace kididdigar yadda suka sarrafa kudadensu na tsawon shekaru.

Wasu daga cikin hukumomin sun hada da: hukumar bunkasa bangaren man fetur ta kasa da kamfanin tallata man fetur da kuma hukumar kayyade farashin man fetur.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!