Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Babu mai kara farashin man fetur a yanzu – NNPC

Published

on

Kamfanin mai na kasa NNPC ya bukaci ‘yan Najeriya da su daina gaggawar sayen man fetur don tanadi sakamakon fargabar karin farashin man fetur da ake yi.

Kamfanin na NNPC ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun sa, Dakta Kennie Obateru, ya fitar a Abuja.

Wannan dai ya biyo bayan yadda ake ganin layuka a gidajen mai na kasar nan yayin da wasu gidajen man suka kasance a rufe, sakamakon fargabar da aka shiga na karin farashin man fetur din a karshen makon da ya gabata.

Obateru ya kuma gargadi dillalan man fetur da ‘yan kasuwa da su guji kara farashin man ba bisa ka’ida ba ko kuma boye shi har yayi karanci a kasuwa.

Ya kuma yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da su kara sa ido kan ayyukan ‘yan kasuwar da nufin hukunta wanda aka kama da irin wannan laifi na karin farashin man fetur ko boye shi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!