Connect with us

Labarai

 Zulum sarkin aiki – Inji masu iya magana

Published

on

Daga Nasiru Salisu Zango

farfesa Babagana Umara Zulum shine Gwamna da yanzu ya zama zakaran gwajin dafi a cikin gwamnonin Nigeria.
Kokarinsa da jajircewarsa wajen kare hakkin talaka a salon mulki irin na salihan baya, shine ya zame masa Jari wajen samun karuwa, ba a jihar Borno Kadai ba har ma a Nigeria baki daya.

Gidan radiyon freedom muryar jama’a zai cigaba da kawo muku Shiri na Musamman akan ayyukan Professor Babagana Umara Zulum gwamnan jihar Borno.

za’a yi ne a tasoshin mu dake Kano da Kaduna.

Shirin zaizo da karfe 7.30 na dare a tashar freedom Kaduna, karfe 8 zuwa 10-10:30 na daren Lahadin a tashar Freedom dake Kano.

HON. Tanimu Tahir Mbaya mataimakin gwamnan jihar Borno a Fannin Yada labarai shine ya dauki nauyin kawo shirin.

A kasance damu Dan Jin kokarin Murucin Kan Dutse Bai fito ba sai da ya shirya.

Rubutu daga Nasiru Salisu Zango

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!