Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ba sani ba sabo ga duk wanda ya taka dokar tsaftar muhalli – Ganduje

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce zata samar da hukunci mai tsauri ga direbobin adaidaita sahu dama ɗaiɗaikun jama’a wadanda su ke karya dokar fita a ranakun tsaftar muhalli na karshen kowane wata.

Kwamishinan muhalli na jihar Kano Dr Kabiru Ibrahim Getso ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan kammala zagayen duban tsaftar muhalli a titunan jihar Kano.

Ya ce, kowane wata sun lura da yadda direbobin babura masu ƙafa uku ke watsi da dokar hana zirga-zirga a lokacin tsaftar muhallin, duk da yarjejeniyar da ake ƙullawa tsakanin ma’aikatar muhalli da shugabannin su.

Getso, ya ƙara da cewa, har yanzu mutane ba su ɗauki tsaftar muhalli da muhimmanci ba ta yadda su ke yawace-yawace a gari a lokacin da ya kamata su tsaftace muhallansu.

Wasu direbobin babura masu ƙafa uku da suka karya dokar a yau sun gurfana a gaban kotun tafi da gidanka karkashin mai sharia Auwal Yusuf Sulaiman.

Wakiliyar mu Madina Shehu Hausawa ta rawaito cewa, ma’aikatar muhalli ta yabawa al’ummar unguwar Ƙofar Nai’sa bisa gudanar da aikin gayya da su ka yi a safiyar yau.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!