Labarai
Gwamnatin Kano ta tabbatar da samun ci gaba a manyan ayyukan raya kasa

Ma’aikatar bibiya da lura da aiyyukan Gwamnatin Jihar Kano, ta tabbatar da samun ci gaba a wasu manyan ayyukan raya kasa da ake gudanarwa a fadin birnin Kano, biyo bayan ziyarar aiwatar da su karkashin jagorancin Kwamishinan ma’aikatar , Kwamared Nura Iro Ma’aji Sumaila.
Ma’aikatar, ta ce aikin gyaran Babbar Masallacin Juma’a na Kano ya kai matakin karshe, Sai dai bayan ruwan sama na farko a bana, an samu zubar ruwa a wasu sassan rufin masallacin, da Sarkin Ladanan Kano ya gabatar da korafin gyaran hakan inda Kwamishinan ya tabbatar da cewa za a sanar da dan kwangilar domin gyara matsalar kafin kammala aikin.
Kwamitin bibiyar ayyukan ya kuma duba aikin fadadawa da gyaran Asibitin Yara na Hasiya Bayero da ke Kofar Kudu, ciki har da cibiyar kula da masu cutar sikila ta Abba Care, sashen kula da masu fama da rashin abinci mai gina jiki da kuma bangaren raba magunguna kyauta.
Kwamishinan ya ziyarci gidan adana kayan tarihi na Gidan Dan Masani, inda ya bayyana gamsuwa da aikin wajen kana ya duba wasu ayyuka da suka hada da gina katanga da saka fitilu masu amfani da hasken rana a Dutsen Dala, gyaran Kwalejin Addinin Musulunci ta Abdullahi Bayero da Makarantar larabci ta (SAS), da kuma shimfida kwalta a hanyoyin Sokoto Road, Iyaka Road, Guda Abdullahi Road, Justice Dahiru Mustapha Road da hanyar Unguwa Uku zuwa Zaria Road ta ‘Yan Awaki.
Nura Iro Ma’aji Sumaila, ya duba manyan ayyuka guda 12 da darajar su ta haura sama da naira biliyan 21.
You must be logged in to post a comment Login