Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ƴan sandan Kano sun cafke mutumin da ya banka wuta a Masallaci

Published

on

Ƴan sanda a jihar Kano sun cafke wani mutum mai suna Shafi’u Abubakar mai shekaru 38 bisa zarginsa da banka wuta a Masallaci yayin da ake tsaka da yin Sallar Asuba.

Rahotonni sun bayyana cewa, mutane sama da 20 ne suka jikkata ciki har da shi mai kunna wutar.

Rundunar ƴan sandan ta bayyana cewa, binciken farko da ta gudanar ta gano cewa mutumin ya banka wutar ne biyo bayan rikicin gado da suke yi na shi da ƴan uwansa.

Sai dai daga bisani limamin Masallacin tare da ƙarin mutum biyu sun rasu a asibitin ƙwararru na Murtala.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!