Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu yi hadin guiwa da wani kamfanin aikin tsaftar muhalli a Kano – Ganduje

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta sahale ma’aikatar muhalli da hukumar kwashe shara REMASAB su yi hadin gwiwa da wani kamfani da ke aikin tsaftace muhalli, wanda zai taimaka wajen inganta harkokin tsaftar muhalli a Kano baki daya.

Kwamishinan muhalli Dakta Kabiru Ibrahim Getso ne ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi, jim kadan bayan kammala zagayen duban tsaftar muhalli na karshen wata.

“A zaman majalisar zartarwa ta jihar Kano Gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya amince ma’aikatar muhalli ta yi hadin gwiwa da kamfanin don kyautata zaftar muhalli a jihar”.

“Muna da tabbacin cewa wannan kudiri zai fara aiki a watan Mayu mai kamawa don, wanda zai ba mu damar fito da tsare-tsare masu inganci na tsaftar muhalli” a cewar kwamishinan.

Dakta Kabiru Ibrahim Getso ya ce, za a kaddamar da fara aikin hadaka da kamfanin ne a watan gobe, wanda mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osibanjo da ministan muhalli Mohammad Mahmood Abubakar za su kaddamar.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!