Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar tattalin arziki tayi Kira ga NEMA ta gaggauta raba kayan abincin a Nijeriya

Published

on

Majalisar tattalin arziki ta kasa da yi Kira ga hukumar bada again gaggawar ta Nijeriya NEMA da ta gaggauta fitar da kayan hatsi zuwa garuruwa, don ragewa Al’ummar kasar tsadar kayan masarufi da ake fama dashi a kasar nan.

Gwamnan jihar Bauchi Bala Abdulkadir Muhammad ne ya bayyana hakan Jim kadan bayan fitowa daga ganawar majalisar tattalin arzikin jiya Alhamis karkashin jagorancin mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima a fadar Aso Rock dake Abuja.

Ya ce ‘mataimakin shugaban kasar ya baiwa hukumar ta NEMA umarnin gaggauta fitar da hatsin tare da hada gwiwa da jihohi a yayin rabon.

Da yake bayyana damuwar sa game da tsadar kayan masarufi, gwamna Bala Abdulkadir ya ce ‘batun abinci ba abu ne da za’a yi wasa da shi ba, a don haka ne ma ya sanya majalisar daukar wannan mataki, baya ga fitar da karin wasu tsare tsare da zasu taimaka a sauran bangarori na walwala da cigaban al’umma’.

Rahoton: Mukhtar Ahmad Birnin Kudu

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!