Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Karota ta kama matasa da buga takaddun bogi a Kano

Published

on

Hukumar kula da zirga zirgar Ababen Hawa ta Kano (KAROTA) ta samu nasarar kama wasu matasa masu buga takaddun bogi tare da siyarwa Direbobi masu daukar kaya (Way Bill) a wasu sassan titunan jihar Kano.

Shugaban Hukumar KAROTA Injiniya Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana hakan ta bakin Kakakin Hukumar Nabilusi Abubakar Kofar Na’isa.

Hukumar ta ce yanzu haka matasan sun shiga hannunta, idan kuma sun kammala bincike za su mika su ga Jami’an ‘Yansandan domin fadada bincike tare da daukar Matakin da ya dace

Hukumar ta cigaba da cewa a baya an sha samun Korafe-korafe makamanta wannan sai yanzu Allah ya ba su nasarar Cafke wadanda ke buga way bill din na bogi tare da siyarwa da direbobi.

Karota ta ja hankalin Direbobi da su kula sosai don kaucewa fadawa hannun bata gari masu wannan mummunar ta’ada, ta kuma sha alwashin cewar ba za su bar duk wanda ke ƙokarin yi wa Hukumar zagon ƙasa a ayyukanta ba a fadin Jihar.

Rahoton: Abubakar Tijjani Rabi’u

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!