Connect with us

Labarai

Ɗan gidan Aminu Abdussalamu ya yi karar Sunusi bature

Published

on

Dan gidan tsohon mataimakin gwamna Kwamared Aminu Abdussalamu Gwarzo, Alhaji Mujahid Aminu Abdussalamu Gwarzo, ya yi karar Daraktan yada labaran gwamnan Kano Sunusi bature Dawakin Tofa a ofishin kwamishinan Yan Sanda bisa zarginsa da yi wa tsohon mataimakin gwamnan kazafi.

Lauyan dan gidan tsohon mataimakin gwamnan Barista Nazifi Mustapha Goron Dutse ne ya bayyana hakan ga Freedom Radio bayan da ya shigar da ƙarar ta cikin takardar da ya kai ofishin kwamishinan a yau Laraba.

Ya ce, sun yi karar Sunusi bature Dawakin Tofa, ne bisa zarginsa da yi wa Kwamared Aminu Abdussalamu Gwarzo, kazafin cewa ya na karbar kudade daga kananan hukumomin jihar Kano 44 lokacin da ya ke da mukamin kwamishina.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!