Labarai
Jirgin Alhazan farko na Kano za su taso daga ƙasa mai tsarki a gobe Juma’a

Har kawo wannan lokaci da muka sami wannan rahoton babu wata sanarwa a hukumance da ta tabbatar da hakan, sai dai wakilin mu Abdurrahman Hamisu Namadina da ke can ya tabbatar da cewa tuni aka fara kwashe jakunkunan alhazan zuwa filin tashi da saukar jiragen sama na Jidda inda ta can Alhazan za su taso.
A hannu ɗaya kuma su ma shugabannin Alhazai na ƙananan hukumomi sun umarci kowane Alhaji da Hajiya su je su yi Ɗawafin bankwana kafin karfe 12 na daren yau Alhamis.
You must be logged in to post a comment Login