Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kungiyar boko haram ta kai hari karamar hukumar Madagali a jihar Adamawa

Published

on

Kungiyar Boko Haram ta kai hari kan al’ummar karamar hukumar Madagali dake jihar Adamawa a daren jiya Litinin, yayin da suka tarwatsa ‘yan sanda dake kan aiki, da kuma tada hargitsi a cikin garin.

Wani jami’In tsaro da ya nemi a saka sunan sa, ya bayyana wa manema labari  da safiyar yau cewa ‘yan kungiyar Boko Haram sun kashe mutum 3, da lalata shaguna 20 da motoci 3 yayin da suka kwashe kayayyakin abinci.

Jami’in tsaron ya ce daga cikin yankunan da abun ya shafa akwai Shuwa da Kirshingari da kuma Shuari.

Sai dai kwamandan rundunar ta 28 dake Mubi Lut Kanal Haruna ya ce tuni sojojin kasar nan suka maida martani kan harin

Yayin da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa Othman Abubakar ya bada tabbacin cewa tuni hukumomin tsaro suka maido da zaman lafiya a yankin.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!