Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

KannyWood

A shirye nake na auri Kamaye a zahiri –inji Adama

Published

on

Fitacciyar jarumar fina-finan Hausar nan Zahra’u Saleh wadda akafi sani da Adama matar Kamaye acikin wasan kwaikwayon nan na Dadin Kowa ta bayyana cewa a shirye take da ta auri abokin karawarta a wasan kwaikwayon wato Dan’azimi Baba Chediyar ‘Yan Gurasa wanda akafi sani da Kamaye.

A yayin wata tattaunawa da Freedom Radio tayi da jarumar a jiya Laraba Adama ta bayyana cewa “shi aure al’amari ne na Allah, kuma idan Allah ya rubuta cewa Kamaye mijina ne to hakika sai na aureshi, kuma ba abin mamaki bane domin kuwa a shirye nake da na aureshi”

Jaruma Adama ta kara da cewa ita sam ba mafadaciya bace a zahiri, kawai dai wasa ne aka bata tsarin ta fito a matsayin mafadaciya, a karshe tayi kira ga sauran jaruman masana’antar Kannywood da su taimaka su hada kansu su kaucewa rikice-rikice domin tabbatar da zaman lafiya da cigaba ga jaruman da masana’antar su.

Labarai masu alaka:

‘Yan film sun karrama kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano

Ina so na zama ‘yar kasuwa kamar Dangote –Sadiya Kabala

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!