Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

KannyWood

Tabbas Afakallahu na kokari wajen tsaftace Kannywood –Kamaye

Published

on

Fitaccen jarumin fina-finan hausar nan kuma marubuci mai shirya fina-finai Dan’azimi Baba wanda akafi sani da kamaye, ya bayyana cewa yanzu haka masana’antar Kannywood ta kama hanyar gyaruwa sakamakon kokarin hukumar tace fina-finai ta jihar Kano.

Yayin wata tattaunawa da jarumin yayi da Freedom Radio ya bayyana cewa a yanzu masana’antar Kannywood ta dauko hanyar gyaruwa bisa kokarin da shugaban hukumar tace fina-finai da daba’I ta jihar Kano Alhaji Isma’il Na’abba Afakallah ke yi.

Kamaye ya kara da cewa yana goyon bayan yunkurin tsaftace fina-finan hausa dari bisa dari da Afakallahun ke yi a Kano.

Idan zaku iya tunawa a kwanakin baya ne dai wata dambarwa ta kunno kai tsakanin wasu jaruman masana’antar da suke zargin ana musu rashin adalci, a yayin ayyukan hukumar tace fina-finan ta jihar Kano.

Wannan dambarwar dai ta haifar da ficewar wasu jarumai daga masana’antar baki daya.

Labarai masu alaka:

Mu mukayi sakaci Kannywood ta lalace –Kamaye

A shirye nake na auri Kamaye a zahiri –inji Adama

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!