Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

KannyWood

Mu masu gyaran tarbiyya ne –Teema Makamashi

Published

on

Fitacciyar jarumar fina-finan Hausar nan Teema Makamashi ta karyata rade-radin da ake yadawa na cewa jaruman masana’antar Kannywood basu da tarbiyya.

Yayin wata tattaunawa da jarumar tayi da Freedom Radio ta bayyana cewa “Mu muke da tarbiya, saboda mu muke bada gudummuwa wajen gina tarbiyar ‘ya’yan mutane, na san wadanda suke yawace-yawacen sata, da karuwanci amma sanadiyar wani film da suka kalla sun daina”.

Teema Makamashi ta kara da cewa mafi yawa bakin haure a masana’antar ne ke bata musu suna, amma su ‘yan film mutane ne masu daraja da tarbiyya.

Sannan jaruma Teema Makamashi ta ja hankalin jaruman masana’antar Kannywood kan su daina yiwa juna hassada domin hakan na daya daga dalilan dake kawo cikas ga cigaban masana’antar.

Rubutu masu alaka:

‘Yan film sun karrama kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano

Ina so na zama ‘yar kasuwa kamar Dangote –Sadiya Kabala

A shirye nake na auri Kamaye a zahiri –inji Adama

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!