Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Da dumi-dumi: Hisbah ta janye dokar hana cakuda maza da mata

Published

on

Rahotonni daga fadar gwamnatin jihar Kano na cewa tuni gwamnati ta janye dokar nan ta hana cakuda maza da mata a baburan adai-daita sahu.

Wata majiya mai tushe daga fadar gwamnatin jihar Kano ta shaidawa Freedom Radio cewa anyi wani kwarya-kwaryar zama na musamman a yau Litinin tsakanin masu ruwa da tsaki a al’amuran addini a jihar Kano kan fara aiwatar da wannan doka, inda zaman ya cimma matsayar janye dokar har zuwa wani lokaci.

Freedom Radio ta nemi jin ta bakin babban kwamandan hukumar Hisbah ta jihar Kano, Sheikh Muhammad Haroun Ibn Sina wanda ya ce ayi masa uzri idan Allah ya kaimu gobe Talata zasu gudanar da taron manema labarai kan dokar.

Idan zaku iya tunawa dai hukumar Hisbah ta ce zata jaddada dokar hana cakuda maza da mata a baburan adai-daita sahu daga farkon shekara ta 2020 mai kamawa.

Sai dai batun ya haifar da cece kuce, musamman a kafafan sada zumunta.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!