Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumomi sun rufe asibitin Maita a Kano

Published

on

Hukumar kula da asibitoci masu zaman kansu ta jihar Kano da hadin gwiwar hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano sun rufe wani asibitin Maita da aka bude a nan Kano.

Asibitin wanda Chiroman sarkin mayun Kano, Alhaji Yahya Ali ya bude a garin Gano dake karamar hukumar Dawakin Kudu, ana kwantar da marasa lafiya tare da lura dasu ta hanyar maita.

Wasu majinyata da aka samu a asibitin sun bayyana cewa ana kafa musu kusa tare da zuko ruwa daga cikinsu da sunan yi musu magani.

Sai dai da farko wasu daga majinyatan sunyi kemadagas sunki yarda a dauke su daga asibitin mayun zuwa na gwamnati kamar yadda wakilinmu Aminu Abdu Bakanoma ya rawaito mana.

Kazalika a yayin da aka tura Chiroman Mayun zuwa kotu nan take ya fadi ya kuma marai-raice cikin halin rashin lafiya a harabar hukumar karbar korafe-korafe ta jihar Kano.

Amma tuni jami’an hukumar sun garzaya da shi asibiti domin tabbatar da cewa shin rashin lafiya ce ta zahiri ko kuma kirkirarriya ce.

Idan zaku iya tunawa dai tun a watannin baya ne dai hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ta cafke tawagar sarkin mayun jihar Kano da wasu daga ‘yan majalisarsa wanda cikin binciken da ake musu ya kai ga bankado wannan asibiti.

Labarai masu alaka:

Sarkin mayun boge ya karyata kansa

Mun kama Sarkin mayu na bogi-Muhiyi Magaji

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!