Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Mun samu rahoton aikata ba daidai ba a wasu mazabu-Abdulmumini Jibrin.

Published

on

Daga Abdullahi Isa

Dan takarar jam’iyyar APC a zaben dan majalisar wakilai da ke gudana a yau a yankin kananan hukumomin Kiru da Bebeji, Abdulmumini Jibrin, Kofa, ya ce sun samu labarin aikata laifuffukan zabe a wasu daga cikin mazabun kananan hukumomin guda biyu.

Abdulmumini Jibrin wanda ke zantawa da manema labarai bayan ya kada kuri’arsa a cibiyar zabe ta Kai’lu da ke Kofa a yankin karamar hukumar Bebeji.

Idan ba’a farga ba  Yan siyasa zasu yi amfani da Almajirai a matsayin ‘’Yandaba- Sarki Sunusi II

Shugaba Buhari ya ja kunnen yan siyasa kan yakin neman zabe

”Magana ta gaskiya a wasu mazabun wakilanmu sun tabbatar mana cewa ana aikata abubuwa marasa dadi amma ba zamu ce komai ba kan wannan batu a yanzu sai nan gaba.” inji Abdulmumini Jibrin Kofa.

Sai dai ya ce ya gamsu da yadda zaben ke gudana a mazabar sa saboda komai ya wakana lami lafiya.

Freedom Rediyo ta gano cewa an samu karancin fitowar jama’a a da dama daga cikin mazabun da ke yankunan kananan hukumomin biyu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!