Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Bana neman matar Aure-BABANGIDA

Published

on

Tsohon shugaban mulkin sojin kasar nan janar Ibrahim Badamasi Banagida mai ritaya, ya ce, shi kam baya neman wata matar aure.

A wata zantawa da yayi da jaridar Daily Trust, janar Ibrahim Badamasi Babangida mai ritaya, ya ce, shi ba ya bukatar yin aure a yanzu, saboda duk wata kulawa da ya kamata ‘ya’ya su yiwa mahaifinsu ‘ya’yan sa, na yi masa.

Ya ce, a yanzu  a matsayin sa na dattijo dan sama da shekaru saba’in, yana ga ba ya bukatar sai ya yi aure.

A baya-bayan nan ne dai, rahotanni su  ka yi ta yawo a kafafen yada labarai da ke cewa, tsohon shugaban mulkin sojin na neman matar aure.

A ranar 7 ga watan Disamban shekarar 2009 ne, mai dakin tsohon shugaban kasar, Hajiya Maryam Ibrahim Badamasi Babangida, ta rasu a wani asbiti da ke birnin Los Angles a jihar California da ke kasar Amurka bayan ta yi fama da cutar daji. Tun daga nan dai har ya zuwa yanzu, tsohon shugaban kasar, bai kara yin aure ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!