Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Kano zata dauki matakai tsaurara kan wandada ke kin tsaftace muhallan su

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce zata dau matakai tsaurara kan duk wanda ta sake kamawa da bujirewa na kin tsaftace muhallansu ko harabar sana’arsu.

Babban Sakataren ma’aikatar muhalli na jihar Kano Alhaji Ibrahim Halilu Dan-Tiye ne ya bayyana hakan yayin ran-gadin duba tsaftar muhalli na karshen wata.

Dan-Tiye yace,  a zagayen da tawagar ta yi , masu ababen-hawa da dama da dai-daikun mutane  sun fito suna ta hada-hada su a maimakon tsaftace muhalli.

Wasu daga cikin mutane da aka ci su tara sun bayyana nadamarsu tare da neman afuwar Gwamnati.

Babban Sakataren ya kuma ja hankalin al’umma da su kasance masu bin doka da oda don kaucewa hukunci.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!