Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar wakilai ta janye dakatarwar da ta yiwa Abdulmumin Jibrin kofa

Published

on

Majalisar wakilai ta janye dakatarwar da ta yiwa dan majalisa mai wakiltar Kiru da Bebeji daga jihar Kano Abdulmumin Jibrin.

Wannan na zuwa ne biyo bayan wasikar ban hakurin da dan majalisar Abdulmumin Jibrin ya aikewa majalisar.

Duk da cewa shugaban majlisar be karanta dukkanin abinda wasikar ta kunsa ba yayin zaman majalisar, sai dai yace ya bawa majalisar hakuri, kuma ya gabatar da duk wasu matakai da majalisar ta bukace shi ya bayar.

A cewar shugaban majalisar Yakubu Dogara bayan ya gama karanta wasikar, majalisar ta bashi damar cigaba da zuwa bakin aikin sa a duk lokacin da yake bukata.

A shekarar 2017 ne majalisar wakilan ta dakatar da dan majalisar Abdulmumin Jibrin halartar duk wani zama da zatayi, sakamakon bayyana zargin da yayiwa majalisar na cewa tayi cushe cikin kunshin kasafin kudi.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!