Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar NDLEA: Sun koka na yadda matasa ke ta’amali da kwayoyin Tramadol

Published

on

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta koka kan yadda matasan kasar nan da kuma Mata ke ta’ammali da Kwayoyin Tramadol da kuma maganin tari na sha.

Shugaban hukumar ta NDLEA Kanar Muhammad Abdallah mai ritaya ne ya sanar da hakan yayin jawabin da ya gabatar kan yadda za a yaki aikata munanan laifuka gami da shan miyagun kwayoyi a Duniya, a babban taron taron zauren Majalisar dinkin Duniya a birnin New York din Amurka.

Kanar Abdallah mai ritaya ya jaddada kudurin kasar nan wajen mara baya ga tanade-tanaden da kasashen Duniya suka yin a yaki da miyagun laifuka da kuma ta’ammali da muggan kwayoyi.

Ya kara da cewa Najeriya ta sake jan damara wjen kawar da mummunar dabi’ar nan ta safarar mutane da yaduwar makamai ba bisa ka’ida ba da kuma dakile ayyukan masu halasta kudaden haram.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!