Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar IOM ta ceto tare da dawo da yan Najeriya 9888 daga kasashe daban-daban

Published

on

Hukumar kula da ‘yan cirani ta duniya (IOM) ta ce ya zuwa yanzu ta samu nasarar ceto ‘yan kasar nan dubu tara da dari takwas da tamanin da takwas tare da dawo da su gida daga kasashe daban-daban.

Babban jami’in hukumar Frantz Celestin ne ya bayyana hakan yayin wata ziyara da ya kai wa hukumar yaki da masu safarar bil’adama ta kasa (NAPTIP) jiya a Abuja.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’ar yada labaran hukumar ta NAPTIP NnekaAniagoh.

Cikin sanarwar hukumar ta (IOM) ta sha alwashin yin aiki tare da hukumar (NAPTIP) domin dakile safarar bil’adama a kasar nan.

Sanarwar ta kuma ruwaito shugabar hukumar yaki da safarar bil’adama ta kasa (NAPTIP) Dame Julie Okah-Donli tana cewa, hukumar tana aiki ba dare ba rana don tallafawa wadanda aka dawo da su daga kasashen ketare don sake dawo da su cikin al’umma.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!