Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mun sa kafar wando daya da masu safarar miyagun kwayoyi a Kano – NDLEA

Published

on

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta ce, yanzu Jihar Kano na matakin na shida a bangaren sha tare da ta’ammali da miyagun kwayoyi idan aka yi la’akari da jihar legas wadda take a mataki na daya.

Babban kwamanda a hukumar reshen jihar Kano, Dakta Ibrahim Abdul ne ya bayyana hakan a yau ta cikin shirin ‘Barka Da Hantsi’ na nan tashar Freedom Radio, wanda ya maida hankali akan matsalar shaye-shaye a fadin kasar nan.

Dakta Ibrahim Abdul ya ce, hukumar ta yi nasarar kama kwayoyi da aka shigo da su daga wasu ‘yankuna da suka hadar da taban Wiwi bakwai da kuma hodar ibilis guda hudu, sai kuma tramadol da sauraran su.

Karin labarai:

Akwai sauran rina a kaba, a yaki da miyagun ‘kwayoyi a Kano – inji ‘Yan Magani

Da mu za’a kawo karshen shaye-shayen miyagun kwayoyi –ALGON

Hukumar ta kuma koka bisa yadda ta ce kotu na bayar da belin wanda aka kama da shigo da miyagun kwayoyin ba tare da an gama binciken ba.

Kwamandan ya kara da cewa, daga cikin babbar matsalar da hukumar ke fuskanta akwai karancin kayayyakin aiki, wanda ke haifar da koma baya ga hukumar wajen gudanar da aikin ta yadda ya kamata.

Dakta Ibrahim Abdul ya kuma ce, akwai horo mai tsanani akan dukkanin ma’aikacin hukumar da aka kama da taimakon masu shigo da kwayoyin cikin jihar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!