Labarai
A yau za’a gudanar da zaben Gwamna a jihar Osun

A yau Asabar, 15 ga Agusta, dubban daruruwan masu kada kuri’a a Jihar Osun za su fito domin zaben wanda zai jagoranci jihar.
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta shirya gudanar da zaben gwamna a fadin kananan hukumomi 30 dake fadin jihar.
A cikin ’yan takarar da zasu fafata a zaben na yau akwai Gwamna mai ci, Ademola Adeleke na jam’iyyar Accord, Bola Oyebamiji na jam’iyyar APC, da kuma Najeem Salaam na jam’iyyar ADC.
Shugaba Bola Tinubu ya yi kira da a tabbatar da zaman lafiya, tare da bukatar jami’an tsaro su kare masu kada kuri’a da jami’an hukumar zabe mai zaman kanta INEC.
You must be logged in to post a comment Login