Connect with us

Labarai

Atiku ya shigar da kara kotu kan ta hana Tinubu takara a zaben 2027

Published

on

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar, ADC, Alhaji Atiku Abubakar, ya shigar da ƙara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, yana neman a hana Shugaba Bola Ahmed Tinubu tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.

 

Atiku ya ɗauki wannan mataki ne bisa zargin cewa an samu sabanin bayanai da kuma takaddamar sahihancin takardar sallamar hukumar Bautar kasa ta NYSC da ake dangantawa da Shugaba Tinubu.

 

A cikin ƙarar, Atiku ya nemi kotu ta binciki takardun da Tinubu ya gabatar wa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, musamman bayanan da suka shafi takardar NYSC.

 

Ya kuma nemi kotu ta yi amfani da tanadin Kundin Tsarin Mulkin Najeriya da ya shafi rashin cancantar wanda aka tabbatar da cewa ya gabatar da takardar bogi wajen neman takarar shugaban ƙasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!