Connect with us

Labarai

Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON ta sanar da sabbin kudaden aikin Hajjin 2027

Published

on

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta sanar da sabbin kudaden aikin Hajjin 2027 da gwamnatin ta da su, bisa la’akari da farashin ayyuka, canjin kudin waje da jin dadin mahajjatan.

Kudin Hajjin ya bambanta bisa yankunan da kowane Mahajjaci zai tashi, inda mahajjatan Maiduguri da Yola za su biya N7,560,822, na yankin Arewa N7,672,822, yayin da na yankin Kudu za su biya N7,882,822.

NAHCON ta ce wadanda suka riga suka biya N5,000,000 za su biya ragowar kudin domin kammala rajistarsu, yayin da sababbin masu rajista za su biya ta hukumomin jin dadin Mahajjata na jihohinsu ko bankunan da ke cikin tsarin ajiyar kudin Hajji.

Hukumar ta sanya 26 ga Satumba 2026 a matsayin wa’adin karshe na shigar da bayanan biometric na mahajjata cikin manhajar Nusuk-Masar, yayin da jihohi za su kammala tura kudaden Hajjin zuwa 2 ga Disamba 2026. NAHCON ta gargadi cewa ba za a kara wa’adin ba, kuma kasa cika sharuddan na iya janyo asarar guraben Hajjin da aka ware.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!