Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Abin da ya sa muka gaza biyan kuɗin jami’an zaɓe – Farfesa Sheka

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSIEC ta yi ƙarin bayani kan rashin biyan ma’aikatan wucin gadi da suka yi mata aiki lokacin zaɓen da ya gabata.

Shugaban hukumar Farfesa Garba Ibrahim Sheka ya ce, halin matsin tattalin arziƙi da ake ciki shi ne ya haifar da tsaiko wajen biyan ma’aikatan.

Sheka ya bayyana hakan ne ta cikin shirin Barka da Hantsi na nan Freedom Radio da safiyar ranar Alhamis.

A cewar sa, hukumar na jin ba daɗi kan rashin biyan jami’an haƙƙoƙinsu, kuma sun fara biyan wani ɓangaren daga ciki.

Labarai masu alaka:

Rahoto : Ganduje zai kashe fiye da Naira biliyan 2 wajen zaben kananan hukumomin

Siyasar Kano: Mahangar masana kan zaben kananan hukumomi

Ko da aka tambaye shi kan maganar da ya taɓa yi a baya cikin shirin na cewa, Gwamnatin Kano ta basu dukkan kuɗaɗen gudanarwa sai ya musanta hakan.

Sheka ya ce, an bada sahalewar fitar da kuɗin ne ba wai gaba ɗaya kuɗin gwamnati ta biya ba.

A ranar 16 ga watan Janairun da ya gabata ne aka gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin na Kano.

Sai dai har yanzu jami’an wucin gadi da hukumar ta ɗauka suna ci gaba da kokawa kan rashin biyan na su haƙƙoƙinsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!