Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Adadin masu Corona sun haura 100 a jihar Borno

Published

on

Gwamnatin jihar Borno ta tabbatar da cewa yanzu haka mutane 106 aka tabbatar sun kamu da cutar Covid-19 a jihar.

Ma’aikatar lafiya ta jihar Borno ta wallafa a shafinta na Twitter cewa a ranar Talata an samu karin mutane 6 wadanda suka kamu da cutar a jihar, wanda ya kai adadin zuwa mutane 106.

Har ila yau, sanarwar ta kara da cewa izuwa yanzu mutane 14 ne suka rasa ransu sanadiyyar cutar a jihar.

Wakilin mu a jihar Borno Alaji Ibrahim Injiniya ya zanta da kwamishinan lafiya na jihar Dakta Salihu Aliyu Kwaya-Bura wanda ya tabbatar masa da cewa yanzu an sallami mutane 2 na farko da suka warke daga cutar Covid-19 a jihar.

Karin Labarai:

Ma’aikatan lafiya 7 sun kamu da Coronavirus a Borno

Rundunar Soji ta musanta labarin kai hari barikin sojoji a Borno

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!