Connect with us

Labarai

ADC ta ankarar da INEC kan amfani da malaman jami’a masu ra’ayin siyasa

Published

on

Jam’iyyar ADC, ta bukaci Hukumar Zabe ta Najeriya INEC, da ta sake duba batun yin amfani da malaman jami’a da ke da ra’ayin siyasa wajen tattarawa da kuma bayyana sakamakon zaben 2027.

Sakataren Yada Labaran jamiyyar, Bolaji Abdullahi, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar. Ya ce jam’iyyar na nuna damuwa ne bayan rahoton cewa sama da manyan malaman jami’a 600 a arewacin Najeriya sun bayyana goyon bayansu ga Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027.

 

Jam’iyyar ta bukaci INEC ta samar da ka’idojin da za su hana jami’an zabe masu nuna bangaren siyasa gudanar da irin wannan aiki, tare da wallafa sunayen jami’an da za ta nada tun kafin zabe domin a gano duk wani rikicin muradun siyasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!