Connect with us

Labarai

NUP ta yaba wa Shugaba Tinubu kan fara biyan hakkokin tsoffin ma’aikatan Nigeria Airways

Published

on

Kungiyar ‘yan fansho ta Najeriya NUP, ta yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan fara biyan hakkokin tsoffin ma’aikatan kamfanin jiragen sama na Nigeria Airways Naira biliyan 18.

Kungiyar ta ce, kudin zai amfani tsoffin ma’aikata 2,700 da suka shafe sama da shekaru 20 suna jiran hakkokinsu.
Shugaban NUP na ƙasa, Godwin Abumisi, ya ce biyan kudin ya nuna cewa gwamnati ta saurari kiraye-kirayen da kungiyar ke yi na ganin an biya tsoffin ma’aikatan hakkokinsu.

 

Sai dai kungiyar ta bukaci gwamnatin tarayya ta tabbatar da kammala biyan kudin cikin gaskiya da adalci, tare da sake tantance wadanda ba a kammala batunsu ba, musamman wadanda ke da matsalar bayanan asusun banki. Ta kuma nemi a biya hakkokin wadanda suka rasu ga magadansu bisa ka’ida.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!