Labarai
Hukumar Civil Defence ta cafke mutane 13 da ake zargi da aikata manyan laifuka

Hukumar tsaro ta Civil Defence, ta kama mutane 13 da ake zargi da aikata laifukan satar wayoyin wutar lantarki da fashi da makami da kuma satar motoci da safarar mutane.
Jami’in hulda da jama’a na kasa na hukumar, Mataimakin Kwamanda Babawale Afolabi, ne ya bayyana hakan yayin da yake gabatar da wadanda aka kama a hedikwatar hukumar.
Ya ce, an gudanar da kamen ne a Abuja da jihohin Nasarawa da Plateau da Kogi da Benue da Neja da kuma Kaduna.
Ya ce, daya daga cikin wadanda ake zargin, tsohon ma’aikacin kamfanin AEDC mai suna Isaac Zegbe, tare da wasu abokan ta’asarsa da ake zarginsu da lalata sama da kilomita 15 na wayoyin aluminium daga Yangoji zuwa Abaji, wadanda kudinsu ya haura Naira miliyan 350.
Hukumar ta kuma ce, ta kama wasu da ake zargi da fashi da makami, inda ta kwato bindiga kirar AK-47 da harsasai 16 da kuma Naira 70,000.
You must be logged in to post a comment Login